Zargin bata tarbiyya: Sarkin Katsina na shirin korar AGILE daga jihar

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Mai Martaba Sarkin Katsina, Abdulmuminu Kabir, na shirin korar shirin nan na inganta ilmin ’yan mata mai suna AGILE daga fadin jihar.

Sarkin ya ce, shirin na AGILE yana wuce gona da iri da kuma kokarin gurbata tarbiyyar Musulunci da ta al’ada da aka san yankin da ita.

Sarkin ya bayyana haka ne a fadarsa ranar Asabar lokacin da yake aiwatar da wasu nade-nade.

Talla

Kazalika, ya ce shirin yana cin karo da koyarwar addinin Musulunci wanda ya ce a matsayinsu na iyayen al’umma ba za su bari hakan ta faru ba.

Don haka ya ce, lallai ne wannan shiri ya fita daga Jihar Katsina baki daya.

Hukuncin Kotun Koli: ‘Yan sanda sun yi sabon gargadi ga al’ummar jihar Kano

Shiri AGILE na da nufin habaka ilmin zamani na ’yan mata daga karamar makaratun sakandaren zuwa babba, inda ma har ake ba su wani ihisani.

Sai dai wasu masu nazari da suka yi sharhi a kai sun ce shirin in baya ga bata tarbiyya da kokarin sanya daliban bujire wa iyaye da wasu ka’idodi da tarbiyar addini da ta al’ada babu abin da shirin yake koyarwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...