Rufe asusu: Gwamnatin Kano ta mayar da martani

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Gwamnatin jihar kano ta bayyana cewa bata san daga inda aka samo umarnin Kotu na rufe asusun gwamnatin jihar ta Kano ba.

 

Kadaura24 ta rawaito wata sanarwa da ma’aikatar shari’a ta jihar kano ta fitar, tace ta lura da wata takarada dake yawo a shafukan sada zumunta wadanda ke nuna cewa wata Kotu dake Abuja ta umarci da a kulle asusun na gwamnatin jihar sakamakon kin biyan diyyar masu shaguna a filin idi.

 

Sai dai ma’aikatar ta shari’a tace har Yanzu bata samu wannan Hukunci a hukunance ba, wanda shi ne zai gasgata Ingancin hukuncin dake yawo a shafukan sada zumunta.

Talla

Ma’aikatar tace ta umarci lauyoyin su da su gudanar da  bincike akan wanann batu dake yawo a shafukan sada zumunta.

Hukuncin Kotun Koli: ‘Yan sanda sun yi sabon gargadi ga al’ummar jihar Kano

Ranar Laraba ne dai wata Kotun tarayya dake Abuja ta umarci wasu bankuna guda 24 da su rufe asusun gwamnatin jihar kano dake bakunansu sakamakon kin biyan diyyar Naira Biliyan 30 ga masu shaguna a filin masallacin idi na Kofar mata dake Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...