Nasiru Gawuna zai mayar wa yan kasuwar Kano wuraren su da aka rushe musu, in an gama Shari’a – Aruwa

Date:

Daga Abdurrashid B Imam

Shugaban kungiyar shugabannin jami’an hulda da jama’a na jam’iyyar APC dake arewa maso gabas, wanda kuma shi ne kakakin jam’iyyar a Kano Hon. Ahmad S Aruwa ya yi kira tare da jan hankalin yan majalisar jihar kano da kada su kuskura su sahalewa gwamnan kano ta tafi hutun da ya ce za shi.

“Ina tabbatarwa al’ummar jihar kano cewar ko ina Abba ya shiga, indai jam’iyyar APC ta karɓi mulkin jihar kano babu makawa sai mun dawo da shi don ya girbi abinda ya shuka”.

Aruwa ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da yayi da jaridar kadaura24 a kano.

Talla

Hon. Aruwa ya yi alkawarin cewa zasu bayarwa duk dan kasuwar jihar Kano da akai musu rusau da zarar Nasiru Yusuf Gawuna ya tabbata matsayin gwamnan jihar kano nan ba da jimawa zasu maidawa da kowa wajan sa tare da rage musu wani abu daga cikin asarar da akai musu .

NJC ta amince da ƙarin girma ga alkalin da ya yanke hukuncin zaɓen gwamnan Kano a kotun daukaka kara

” Rusau din da wannan gwamnatin ta yi ya dawo da harkokin kasuwanci baya a jihar kano, sannan ya nuna cewa ita wannan gwamnatin ba Mai kishin yan kasuwa da sauran al’ummar jihar kano ba ne”. Inji Aruwa

Daga karshe ya tunasar da al’ummar jihar kano cewa yana da kyau su kara dagewa da yin addu’o’in samun nasara Dr. Nasiru Gawuna a Kotun Ƙoli domin cigaban jihar kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...