Sojin Nigeria sun kama jirgin ruwa dauke dayan man fetur na sata

Date:

Rundunar sojin ruwa ta Najeriya ta kama wani jirgin ruwa ɗauke da gangar mai 3,665 da take zargi na sata ne a yankin Igbokoda na jihar Ondo.

Cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar, ta ce ta kama ma’aikatan jirgin 17, da take zargi da satar man daga rijiyar mai ta Ebesan a ƙaramar hukumar Ilaje da ke jihar.

Daraktan yaɗa labaran rundunar, Commodore Ayo-Vaughan, ya ce an kama jirgin ne a ranar Alhamis.

Talla

Ya ce rundunar ta samu bayanan sirri kan ayyukan mutanen da take zargi da sace man, inda nan take ta tura jami’anta waɗanda suka yi nasarar kama mutanen.

NJC ta amince da ƙarin girma ga alkalin da ya yanke hukuncin zaɓen gwamnan Kano a kotun daukaka kara

Sanarwar ta ce sojojin sun gano cewa an daɗe ana amfani da jirgin wajen satar man daga kowane ɓangare na rijiyar.

Jirgin na da girman da zai iya ɗaukar nauyin metric ton 15,000, kuma a lokacin da aka kama shi yana ɗauke da man da nauyinsa ya kai metric ton 500.

Satar mai a kudancin Najeriya dai wata matsala ce da ta daɗe tana ci wa ƙasar tuwo a ƙwarya, inda ɓata-gari ke sace ɗimbin mai ta hanyar fasa bututan man ko amfani da rijiyoyin mai ba bisa ƙa’ida ba, lamarin da ke ƙara haifar da koma-baya kan tattalin arzikin ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...