Lauyoyi 500 sun yi alƙawarin kare Gawuna a Kotun Ƙoli

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

Kimanin lauyoyi masu zaman kansu 500 ne suka yi alƙawarin kare dan takarar gwamnan Kano a karkashin jam’iyyar APC, Nasir Yusuf Gawuna a kotun koli.

kadaura24 ta rawaito Joseph Onwudiwe, mai magana da yawun lauyoyin a karkashin kungiyar masu kula da dimokuradiyya da doka ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai a Abuja a yau Talata.

Talla

Mista Onwudiwe ya ce an yi hakan ne domin inganta dimokuradiyyar kasar.

“Yan Najeriya sun lura sosai da halin da ake ciki a jihar Kano dangane da zaben gwamnan da aka yi a ranar 18 ga Maris.

Harin Yan Maulidi: Ya’yana 6, duk an kashe su —Magidanci

“A matsayinmu na kungiyar da ke da alhakin kare mutuncinmu da dabi’unmu na dimokuradiyya, yanzu ba mu gamsu da hare-haren maganganu marasa dadi da ake kaiwa bangaren shari’a ba.

“Kuma wani yunƙuri na bata wa Kotun suna ba. Ba za mu sake naɗe hannayenmu a matsayin lauyoyi ba kuma mu kalli yadda ake ci gaba da cin zarafi da cin mutuncin sashen shari’a ba,” in ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ba zaben 2027 ne a gaba na ba – Tinubu

    Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu...

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...