Yadda Tinubu ke shan suka kan tafiya da wakilai sama da 1000 kasar Dubai

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Ana ci gaba da ce-ce-ku-ce dangane da ɗumbin wakilan Najeriya har 1,400 da gwamnatin Tinubu ta tura babban taron Majalisar Dinkin Duniya kan sauyin yanayi na COP28.

Lamarin dai ya janyo jam’iyyar ƴan adawa ta PDP da na Labour fara gudanar da bincike inda suka buƙaci gwamnatin Tinubu ta yi bayani kan wanda ya ɗauki nauyin tawagar Najeriya zuwa taron.

Tun bayan da adadin wakilan kasar ya bayyana, masu suka da jam’iyyun adawa suka yi Allah-wadai da shi, suna masu bayyana rashin jin dadinsu idan aka yi la’akari da yanayin tattalin arzikin kasar.

A cewar PDP, wakilan sun yi yawa matuka inda suka hadar da ƴan baranda da matansu da kuma sauran ƴan ku ci ku ba mu da ke da alaƙa da fadar shugaban ƙasar.

“Jam’iyyar mu tana kalubalantar fadar shugaban kasa da ta bayyana sunayen wakilan jami’an da Gwamnatin Tarayya ta dauki nauyin gudanar da babban taron Majalisar Dinkin Duniya kan sauyin yanayi na Cop28, da yadda irin wadannan mutane ke da alaka da taron, da kuma kudaden da aka kashe wajen daukar nauyin wannan taro ga al’umma.”

Zargin Almundahana: Yan sanda sun kama wani hadimin gwamnan Kano

“Tabbas ‘yan Najeriya na da jerin sunayen wakilan kuma sun san jami’an kananan hukumomi da sauran kungiyoyi masu cin gashin kansu da ya kamata su halarci taron,” in ji PDP a wata sanarwar da ta fitar ranar Lahadi.

‘Yan Najeriya sun cancanci sanin wanda ya bai wa wakilan kasar kudin zuwa taron, kamar yadda kakakin yakin neman zaben jam’iyyar adawa na Labour Party, Yunusa Tanko ya bayyana.

“Abin da muke cewa shi ne lambar wakilan da gwamnati ta dauki nauyi zuwa babban taron Majalisar Dinkin Duniya kan sauyin yanayi na COP28 ya kamata a bayyana wa jama’a don mu sani,” in ji shi ranar Litinin kamar yadda ya shaida wa gidan talabijin na Channels.

“Idan gwamnati na cewa ba ta dauki nauyin daukacin wakilai 1,411 ba, to su ba mu lambar wakilan da gwamnati ta dauki nauyinsu.” In ji Tanko

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...