Kasurgumin Dan daba a Kano Hantar Daba ya mika kansa ga yan Sanda

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Hantar Daba Kwanar Diso ya kai kansa Shelkwatar ‘yan Sandan Kano bayan neman sa da take Ruwa a Jallo.

Kadaura24 ta rawaito mai magana da yawun Rundunar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya sanar da hakan a sahihin shafinsa na Facebook.

Sanarwar tace Hanyar Daba ya Kai kansu Rundunar yan sandan ne bisa rakiyar mahaifiyarsa da yan uwansa a jiya litinin, Inda ya yi alkawarin daina harkokin daba, tare da shan alwashin bada gudunmawa wajen tabbatar da zaman lafiya a jihar kano.

” Ina nadamar abubun da nayi a baya, don haka ina kira ga duk wanda na taba zalunta ta kowacce fuska da ya yafe min, sannan ina rokon rundunar ƴan sandan jihar Kano ta sanya ni cikin wadanda ta ke yiwa afuwa”. A cewar sa

Hanyar Daba ya kuma bada tabbacin cewa yana da yara sama da dari da shi ne shugaban su Kuma ya yi alkawarin kawo su suma su tuba , sannan kuma ba za’a sake samun fadan Daba a unguwar Hausawa Gwale zuwa Kofar Na’isa ba.

Tinubu ya gaji bashin aikin tituna na Naira Tiriliyan 6 daga Gwamnatin Buhari – Ma’aikatar Ayyuka

Sanarwar da kiyawa ya fitar ta nuna cewa yanzu haka hantar daba yana karkashin kulawar rundunar su, don haka duk wanda yasan yana da korafi akan shi to ya je helkwatar rundunar domin abi masa hakkinsa.

Kwamishinan yan Sanda na jihar kano CP Hussaini Gumel ya yabawa al’ummar jihar bisa yadda suke baiwa rundunar hadin kai ta hanyar kai mata sahihan bayanai, Inda ya rokesu da su cigaba da taimakawa rundunar don cigaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...

Kungiyar ’Yan Jaridun Kano Arewa ta Aike da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Alhaji Aminu Dantata

  Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin...

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...