Samar da Ruwa: Gwamnatin Kano ta Fara Ganawa da Masu Ruwa da Tsaki a Bichi

Date:

Daga Abubakar Lawan Bichi

Gwamnatin jihar Kano ta jaddada kudininta na cigaba da Samar da ruwan sha mai tsarta ga Jama’a jahar.

Manajan daratan hukumar Samar da ruwan sha ta jihar Kano Injiniya Garba Ahmad Bichi ya bayyana haka yayi taron masu ruwan da tsaki wand ya kunshi masu unguwani da Yan Kwamitin ruwa na Karamar hukumar Bichi.

Talla

Yace gwamnati jihar Kano ta kashe miliyoyin kudi domin gyara madatsar ruwa ta watari don samar da ruwan ga al’ummar Kananan hukumomin Bagwa,Bichi, Dawaki Tofa, Tsanyawa, da kuma Karamar hukumar Ungogo.

Injiniya Garba Ahmad Bichi ya kara da cewa hukumar samar da ruwa ta jihar Kano ta Shirya taro tartaunawa ga masu ruwa tsaki domin ingarta Samar da ruwan sha ga Jama’a Jaharnan.

Shugaba Tinubu ya Magantu Kan Matsin Rayuwar da yan Nigeria Suke Ciki

Shugaban Kwamiti Samar da ruwan sha na Karamar hukumar Bichi Mallam Aminu Halilu Bichi yace Kwamiti nasu izuwa yanzu ya gyara fayaf fayaf na ruwa wanda suka fashe, ya kuma ce zasu cigaban da ayyuki tukuru domin gani ruwa ya wadata a dukkan fadi Karamar hukumar Bichi.

A Jawabinsa Darata Mai kula da tara kudi na Hukumar ya Samar da ruwa ta Jahar Kano Alh Umar Bala Ibrahim yace Gwamnati Jahar Kano na kashe miliyoyin kudaden domin samar da ruwan sha ga Jama’a, Don haka yayi Kira da Jama’a dasu rika biyan kudin ruwa domin kuwa da kudin ake biyan albashi da kuma gyare gyare a matatu ruwa.

Talla

Taro ya sami halarta dukkan masu ruwa da tsaki aka samar na ruwan sha na Karamar hukumar Bichi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...