Yanzu-Yanzu: Tinubu ya Nada Sabon Shugaban hukumar Aikin Hajji NAHCON

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Shugaban kasar Nigeria Bola Tinubu ya amince da nadin Alhaji Jalal Ahmad Arabi a matsayin shugaban hukumar alhazai ta kasa (NAHCON) na tsawon shekaru hudu (4) .

Shugaban ya umarci shugaban hukumar mai barin gado Alhaji Zikrullah Kunle Hassan ya tafi hutun watanni 3 kafin ya yi ritaya kamar yadda dokar ma’aikatan gwamnati (PSR) 120243 ta tanadar daga ranar 18 ga Oktoba, 2023, wanda ya kai ga a ƙarshe ya yi ritaya daga aiki a ranar 17 ga Janairu, 2023.

Talla

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Shugaban kasa Ajuri Ngelale ya sanyawa hannu kuma aka aikowe manema labarai.

Bude Boda: Yadda Aka Sami Rashin Jituwa A Majalisar Dattawan Nigeria

Sabon Shugaban Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON), Alhaji Jalal Ahmad Arabi, zai fara aiki a ranar 18 ga Oktoba, 2023, kuma zai rike jagorancin hukumar har na tsawon shekaru hudu.

Shugaban kasa Bola Tinubu ya kuma amince da rusye hukumar zartarwa ta NAHCON.

Talla

Shugaban ya yi fatan sabbin shugabannin hukumar ta NAHCON za su yi aiki cikin tsoron Allah tare da kiyaye ka’idojin aiki kamar yadda Alkur’ani mai girma ya fada.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: Bam ya fashe a Kano ya hallaka wasu ya kuma jikkata wasu

Aƙalla mutum biyar ne aka tabbatar da rasuwarsu, yayin...

Kotu a Kano ta sami wani Tela da laifin takurawa makwabtansa da karar keken dinki

Wata kotu a Kano ta samu wani tela da...

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...