Daga Khadija Abdullahi Aliyu
Gwamnan jihar kano Abba Kabir Yusuf ya amince da nadin mutane 10 a matsayin shugabannin hukumomin gwamnatin Kano don cigaba da inganta rayuwar al’ummar jihar kano.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban Sakataren yada labaran gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa kadaura24.

Ga sunayen wadanda aka nada din da hukumomin da aka tura su:
:
1. Hon. Salisu A. Kabo, Director General, Youth Empowerment
2. Dr. Hamisu Sadi Ali, Director General, Debt Management Office
Majalisa ta gargaɗi Tinubu kan kashe kudade ba bisa ƙa’ida ba
3. Abduljabbar Mohammed Umar, Director General, KAN-INVEST
4. Yusuf Kabir Gaya, Executive Chairman, SUBEB
5. Mustapha Adamu Indabawa, Managing Director, Abubakar Rimi Television (ARTV)
6. Hamisu Dogon Nama, Managing Director, Kantin Kwari Market
7. Abdulkadir B. Hussain, Managing Director, Sabon Gari Market
8. Dr Kabiru Sani Magashi, Acting Managing Director, KASCO
9. Aminu Aminu Mai-Famfo, Deputy Managing Director, KASCO
10. Engr, Abubakar Sadiq J. Deputy Managing Director, Kano Line
Gwamnan ya bukaci wadanda aka nada din dasu yi amfani da kwarewar da suke da ita ciyar da ma’aikatun da aka tura su gaba.