Dqga Aisha Aliyu Umar
Abbas Balarabe, wanda aka nada a matsayin minista daga jihar Kaduna, ya yanke jiki ya fadi a yayin tantancewar da majalisar dattawan Najeriya ke yi masa a ranar Laraba.
Mutumin da aka nada a matsayin minista ya fadi a zauren majalisar dattijai wanda ya haifar da firgici a tsakanin ‘yan majalisar.

Balarabe, wanda shugaban kasa Bola Tinubu ya mika sunansa domin maye gurbin tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya fadi ne jim kadan bayan gabatar da kansa a gaban sanatocin.
Yanzu-Yanzu Gwamnan Kano Abba Kabir ya sake sabbin nade-naden mukamai
A ranar Laraba ne majalisar dattawa ta fara tantance sabbin ministoci uku da aka nada.
Wadanda aka nada sune: Dr Jamila Ibrahim, Ayodele Olawande da Abbas Balarabe.