Yanzu-Yanzu: Kotu ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Zaɓen Gwamnan Kano

Date:

Daga Safwan Suraj Iliyas

 

Kotun sauraron kararrakin zabe ta sanya ranar Laraba 20 ga watan Satumba domin yanke hukuncin Shari’ar kujerar Gwamnan Kano.

 

Kadaura24 ta rawaito Idan za’a iya tunawa bayan kammala zaɓen gwamnan jihar kano wanda hukumar zabe ta bayyana Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaben, hakan tasa jam’iyyar APC ta shigar da Kara gaban kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar domin ƙalubalantar zaben.

Talla

A cikin wata sanarwa da ta fito daga Kotu sauraren kararrakin zaben Mai dauke da sa hannun maga takardar kotu , tace za’a gudanar da zaman yanke hukuncin ne a babbar Kotun jihar kano dake Miller Road a Kano.

Da dumi-dumi: Kotu ta yanke hukunci kan zaɓen gwamnan jihar Zamfara

Hukuncin kotun dai shi zai tabbatar da halastaccen wanda ya ci zaɓen, duk kuwa da cewa akwai damar daukaka kara ga duk wanda bai aminta da hukuncin kotun sauraren kararrakin Zaben gwamnan ba .

Yanzu haka dai al’ummar jihar Zamfara suna dakon zuwan ranar litinin din domin hukuncin da kotun zata zartar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...