Yadda wani Mahaifi ya kashe jaririyar kwana ɗaya da haihuwa saboda ya fi son ɗa namiji

Date:

 

Wani matashi dan shekara 28, mai suna Misbahu Salisu, ya kashe jaririyar da aka haifa masa, kwana ɗaya da haihuwa, saboda ya fi son ya samu da namiji.

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ce ta kama mutumin da ke zaune a Doka Baici a karamar hukumar Tofa a ranar Juma’a.

 

Hukumar ta sanar da kama shi ne a cikin wata sanarwa da mataimakin kwamandan rundunar ɓangaren sintiri Mujahid Aminudeen ya fitar a Kano.

Talla

Aminudeen ya ce wanda ake zargin ya sanar da jami’an hukumar cewa ya bai wa jaririyar fiya-fiya shine ta rasu.

Yanzu-Yanzu: Tinubu ya sake nada sabbin ministoci guda 2

Salisu ya kuma baiwa mahaifiyar jaririyar mai suna Sa’ade kwaya a ciki shayi, inda bacci ya kwashe ta kafin ya aikata laifin.

 

“Wanda ake zargin ya amsa laifinsa, inda ya ce ya fi son ɗa namiji ne amma matarsa ​​ta haifi mace, wanda hakan ya sa ya kashe jaririyar,” in ji jami’in a cikin sanarwar.

Ya ce an mika wanda ake zargin ga ‘yan sanda domin gudanar da bincike da gurfanar da shi gaban kuliya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...