Yadda wani Mahaifi ya kashe jaririyar kwana ɗaya da haihuwa saboda ya fi son ɗa namiji

Date:

 

Wani matashi dan shekara 28, mai suna Misbahu Salisu, ya kashe jaririyar da aka haifa masa, kwana ɗaya da haihuwa, saboda ya fi son ya samu da namiji.

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ce ta kama mutumin da ke zaune a Doka Baici a karamar hukumar Tofa a ranar Juma’a.

 

Hukumar ta sanar da kama shi ne a cikin wata sanarwa da mataimakin kwamandan rundunar ɓangaren sintiri Mujahid Aminudeen ya fitar a Kano.

Talla

Aminudeen ya ce wanda ake zargin ya sanar da jami’an hukumar cewa ya bai wa jaririyar fiya-fiya shine ta rasu.

Yanzu-Yanzu: Tinubu ya sake nada sabbin ministoci guda 2

Salisu ya kuma baiwa mahaifiyar jaririyar mai suna Sa’ade kwaya a ciki shayi, inda bacci ya kwashe ta kafin ya aikata laifin.

 

“Wanda ake zargin ya amsa laifinsa, inda ya ce ya fi son ɗa namiji ne amma matarsa ​​ta haifi mace, wanda hakan ya sa ya kashe jaririyar,” in ji jami’in a cikin sanarwar.

Ya ce an mika wanda ake zargin ga ‘yan sanda domin gudanar da bincike da gurfanar da shi gaban kuliya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...