Ƙarin bayani akan dalilin gwamnatin Kano na korar kwamishinan da Oga Boye

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya sallami kwamishinan filaye da safiyo na gwamnatin jihar, Adamu Aliyu Kibiya daga muƙaminsa, bayan zargin sa da furta kalaman tunzura al’umma.

Bugu da ƙari sallamar ta shafi mai bai wa gwamnan shawara kan harkokin wasanni da matasa,Yusuf Imam, wanda aka fi sani da Ogan Boye wanda shi ma ake zargi da furta kalaman da ba su dace ba a madadin gwamnatin.

Talla

A ƙarshen makon nan ne bidiyon jami’an gwamnatin suka rinƙa yawo a shafukan sada zumunta, inda suke furta kalamai game da shari’ar da ake yi kan zaɓen gwamnan jihar da ya gabata.

A cikin wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labarai na jihar, Baba Halilu Ɗantiye da kuma na shari’a Haruna Isa Dederi suka karanta a daren ranar Alhamis, sun ce jami’an gwamnatin sun yi magana ba tare da izinin gwamna ba, sun kuma yi kalamai na tunzura al’umma sannan kuma sun ci zarafin mataimakin shugaban ƙasar, Kashin Shettima.

A cikin kwanakin nan dai yanayin na siyasa ya ƙara zafafa gabanin hukuncin kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓen gwamna na jihar.

Manyan jam’iyyu a jihar, NNPP da APC sun gudanar da addu’o’i da azumi domin neman nasara a shari’ar.

A baya dai ɗaya daga cikin alƙalan kotun ta yi zargin cewa akwai wasu da ke yunƙurin bai wa alƙalai da lauyoyin kotun cin hanci domin samun nasara a shari’ar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...

Zargin kisa a R/Zakara: Gwamnatin Kano za ta kafa kwamiti – Waiya

Gwamnatin jihar Kano, ta ce za ta gudanar da...