Rashin isassun yan sanda ne yake dakile yunkurin mu magance matsalar tsaro a Nigeria – Babban Sufeton

Date:

 

Babban Sufeton ‘yan sandan Najeriya, Olukayode Egbetokun ya ce rashin isassun ‘yan sanda, na kawo wa rundunarsu tarnaƙi wajen daƙile aikata laifuka a faɗin ƙasar.

 

Da yake gabatar muƙala – ga manyan jami’ai masu halartar kwas na 45 a cibiyar tsara manufofi da dabarun shugabanci ta Kuru a jihar Filato – Mista Egbetokun ya ce rundunar na buƙatar ƙarin ‘yan sanda 190,000 domin tabbatar da ayyukanta na tsaron rayuka da dukiyar al’umma a cikin gida.

Talla

Ya ce a yayin da Majalisar Dinkin Duniya ta tanadi cewa kamata ya yi ɗan sanda ɗaya ya kula da mutum 460, a Najeriya ɗan sanda ɗaya na kula da mutum 650 ne.

“Don haka rundunar ‘yan sanda na buƙatar ƙarin jami’ai 190,000 domin kai wa ga mizanin da Majalisar Ɗinkin Duniya ta tanada,” in ji shi.

Gwamnatin Kano ta Magantu kan Zargin yanka Tashar Mota ta Rijiyar Zaki

Babban Sufeton ‘yan sandan ya ce idan ‘yan sanda ba su wadaci ƙasa ba, ba za a iya cimma burin manufofin gwamnati ba.

“Don haka, rashin wadatattun jami’ai, zai iya kawo cikas ga tabbatawar manufofin gwamnati,” in ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar kula da almajirai ta Kasa ta kaddamar da yiwa almajirai Rijista a Kano

Daga Saminu Ibrahim Magashi   Hukumar kula da almajirai da yaran...

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban ƙasa – Barau Jibrin

Daga Isa Ahmad Getso Mataimakin shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Sanata...

Inganta tsaro: Shugaban K/H Tarauni ya ba da fili domin gina ofishin Civil Defence a karkasara

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Shugaban karamar hukumar Tarauni, Alhaji Ahmed...

Gwamnan Kano ya yi sabbin nade-nade

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya nada Malam...