Juyin Mulkin Nijar: Allah ya sake nuna darajar Malamanmu – Ma’aji Babba na Ƙasar Hausa

Date:

Daga Abdullahi Umar

 

Alhaji Salisu Abubakar Khiddir, Ma’ajin Babba na kasar Hausa ya yaba rawar da malaman addinin musulunci na Nigeria suka taka wajen shawo kan sojojin da suka yi juyin mulki a Jamhoriyyar Nijar har suka yarda zasu zauna zama sulhu da Kungiyar ECOWAS.

 

” Allah ne ya kara nunawa duniya muhimmanci da darajar Malamanmu, wadanda suka warware matsalar da barazana da bakin bindiga ta kasa warwarewa, hakan ya kara nuna kimar malaman mu”.

Talla

Alhaji Salisu Abubakar Khiddir wanda wakilin ne ga Mai Martaba Sarkin Daura ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da yayi da wakilin Kadaura24 a kano.

Shari’ar zaɓe: Gwamnatin Kano ta Magantu kan Cin hancin da aka yi yunkurin baiwa alƙaliya

Ma’aji Babba na kasar Hausa yace wannan nasara da malaman suka Samar ba ta samu ba sai da suka hada kansu wajen ajiye banbancin akida da fahimaya, Kuma “Babu shakka da zasu cigaba da hade hankansu wallahi Babu abun da zasu sanya a gaba ba su sami nasara ba”

Juyin Mulki: ECOWAS ta Magantu kan batun Gurfanar da Bazoum a gaban kotu

” Dama mu mun dade da Sani malamai suna da kima kawai rashin hade kansu ne yake jawo matsalolin da har jahilai wadanda basu Kai ba suke fada musu maganganun da basu dace ba, amma idan suka sassauta sukar junansu za’a sami daidaito kuma jahilai su daina cin zarafinsu”. Inji Ma’aji Babba na kasar Hausa

Basaraken ya kuma bukaci yan siyasa da su daina Sanya Malamai a cikin harkokin su na siyasa, suma kuma malaman ya ce bai dace su rika amfani da wuraren karatunsu da mumbarinsu wajen shiga sha’anin Siyasa don kaucewa wulakanci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...