Sauya Sheka: Wike Ya Ziyarci Ganduje

Date:

Sauya Sheka: Wike Ya Ziyarci Ganduje

 

Tsohon gwamnan jihar Ribas kuma wanda za’a nada a matsayin minista, Nyesom Wike, ya ziyarci shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abdullahi Umar Gnaduje, a Abuja, ranar Talata.

 

Wike, wanda ya yaƙi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, a zaben 2023, ya sha musanta yunkurin shiga jam’iyya mai mulki ta APC.

Talla

A yayin wani taron godiya da aka shirya domin karrama shi jim kadan bayan mika mulki a Rivers, Gwamna Simi Fubara ya roki Wike da kada ya watsar da shi kod bayan ya shiga jam’iyya mai mulki.

Ganduje Ya Bukaci ‘Yan Majalisun APC Na Kano Su Goyi Bayan Gwamna Abba Gida-gida

“Muna ganin alamar cewa kamar kana so ka tafi ka barmu a wannan jam’iyyar, to idan ka tafi don Allah kada ka yi min nisa, kasancewar ku irin ku a kusa da ni zai taimakamin wajen yin abun da zai sa jihar mu ta cigaba”.in ji Fubara.

Da dumi-dumi: Kamfanin NNPC ya Bayyana Matsayarsa Kan Batun Kara Kudin Mai Fetur a Nigeria

Hasashen Wike zai fice daga jam’iyyar adawa ya kara karfi ne bayan da shugaba Bola Tinubu ya mika sunan sa ga majalisar domin nada shi a matsayin minista a gwamnatin sa.

Shugabannin jam’iyyar PDP sun nuna rashin jin dadinsu kan hakan tare da yin tunanin matakin hukunta tsohon gwamnan na Rivers.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...

Ciyaman din Wudil ya kaddamar da aikin gina magudanan ruwa a wasu garuruwa a yankin

Daga Maryam Adamu Mustapha   Shugaban karamar hukumar Wudil, Hon. Abba...