Ganduje Ya Bukaci ‘Yan Majalisun APC Na Kano Su Goyi Bayan Gwamna Abba Gida-gida

Date:

Daga Kamal Yahaya Zakaria

 

Shugaban jam’iyyar APC ta kasa, Dakta Abdullahi Ganduje a ranar Litinin ya bukaci ‘yan majalisar dokokin jihar Kano su 14 na jam’iyyar da su marawa gwamnan jihar, Alhaji Abba Kabir Yusuf baya domin cigaban jihar.

 

Abba Kabir Yusuf wanda shi ne gwamnan jihar kano a jam’iyyar adawa ta NNPP , sun adawar siyasa da tsohon gwamnan jihar Abdullahi Ganduje.

Talla

Sai dai yayin da ya karbi bakuncin ‘yan majalisar a wata ziyarar taya murna da suka kai masa a gidan ‘Buhari House’ inda nan ne Sakatariyar jam’iyyar APC ta kasa, Ganduje ya ce goyon bayan gwamnan jam’iyyar adawa ba zai hana su kasancewa ‘yan APC.

“Hakan ba zai hana ku ci gaba da rike matsayin ku na ‘yan majalisar jiha ba, bai hana mu hada kai don samun gwamnatin APC a jihar Kano ba. Abu mafi muhimmanci shi ne al’ummar jihar Kano su samu ribar dimokuradiyya”. Inji Ganduje

Yan sanda sun kama mutane 6 da ake zargi da yin kalaman da basu dace ba ga Sarkin Kano

“Ina so ku yi aiki da gwamnati cikin lumana a jihar Kano, ina kuma tabbatar muku da cewa za mu ba ku kwarin guiwa ta yadda za mu samu karin ‘yan majalisar dokokin jihar da ma har sai mun samu gwamnan jam’iyyarmu.

“Ina taya ku murnar lashe zaben ku da kuma yadda kuka taimaka wa shugaban kasa ya ci zabensa. Shugaban kasa ya nuna ya zuwa yanzu yana daukar jihar Kano da muhimmanci ta hanyar goyon bayan mataimakin shugaban majalisar dattawa daga Kano, ministoci biyu ya nada, sannan muka sami Shugaban kwamitin kasafin kudi na majalisa, uwa uba kuma ya dauko Shugaban Jam’iyya ya bamu, kun ga wannan kadai ya Isa ya nuna muku yadda Shugaban ƙasar ya bamu a Kano, domin ya san idan ya na neman kuri’a a lokacin zabe zai iya zuwa Kano,” inji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...