Da dumi-dumi: Kamfanin NNPC ya Bayyana Matsayarsa Kan Batun Kara Kudin Mai Fetur a Nigeria

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Kamfanin kula da albarkatun man fetur na kasa NNPC ya bayyana cewa bashi da wani shiri na Kara kudin litar man fetir a Nigeria.

 

Idan za’a iya tunawa a makon da ya gabata wasu kafafen yada labarai a Nigeria sun rawaito cewar akwai yiwuwar za’a Kara litar man fetir daga Naira 620 zuwa Naira 720 .

Talla

Kadaura24 ta rawaito kamfanin NNPC ya bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da kamfanin ya wallafa a sahihin shafin sa na Twitter.

Ganduje Ya Bukaci ‘Yan Majalisun APC Na Kano Su Goyi Bayan Gwamna Abba Gida-gida

“Ya ku abokan huldar mu, mu kamfanin NNPC ba mu da wani kudiri na kara kudin man fetur a Nigeria, kamar yadda wasu suke ta yadawa jita-jita. Ku cigaba da sayan ingantaccen man da muke kawo muku cikin farashin da kuka Sani Mai sauki a duk gidajen mai dake fadin Nigeria”. Inji NNPC

Kamfanin ya bukaci al’ummar Nigeria da su yi watsi da waccen jita-jita da ake yadawa saboda ba ta da tushe ballantana makama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...