Da dumi-dumi: Kamfanin NNPC ya Bayyana Matsayarsa Kan Batun Kara Kudin Mai Fetur a Nigeria

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Kamfanin kula da albarkatun man fetur na kasa NNPC ya bayyana cewa bashi da wani shiri na Kara kudin litar man fetir a Nigeria.

 

Idan za’a iya tunawa a makon da ya gabata wasu kafafen yada labarai a Nigeria sun rawaito cewar akwai yiwuwar za’a Kara litar man fetir daga Naira 620 zuwa Naira 720 .

Talla

Kadaura24 ta rawaito kamfanin NNPC ya bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da kamfanin ya wallafa a sahihin shafin sa na Twitter.

Ganduje Ya Bukaci ‘Yan Majalisun APC Na Kano Su Goyi Bayan Gwamna Abba Gida-gida

“Ya ku abokan huldar mu, mu kamfanin NNPC ba mu da wani kudiri na kara kudin man fetur a Nigeria, kamar yadda wasu suke ta yadawa jita-jita. Ku cigaba da sayan ingantaccen man da muke kawo muku cikin farashin da kuka Sani Mai sauki a duk gidajen mai dake fadin Nigeria”. Inji NNPC

Kamfanin ya bukaci al’ummar Nigeria da su yi watsi da waccen jita-jita da ake yadawa saboda ba ta da tushe ballantana makama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...