Ƴan majalisa ɓangaren marasa rinjaye a Ghana sun nuna adawa kan matakin da Ecowas a ɗauka na shirin afka wa Nijar a matsayin wani yunkuri na dawo da mulkin dimokuraɗiyya a ƙasar.
Nijar.
“Majalisar dokokin Ghana ba ta tattauna ba kan lamarin kamar yadda sauran ƙasashe suka yi har ma da ɗaukan mataki, in ji Samuel Ablakwa, wani ɗan majalisa a kwamitin kula da harkokin ƙasashen waje.

Ƴan majalisar sun gargaɗi Shugaban ƙasar, Nana Akufo-Addo cewa ya dakatar da shirin tura sojojin ƙasar domin zuwa
Ya ce Shugaba Akufo-Addo ba sai ya ji ta baki ƴan ƙasar Ghana ba kan lamarin , saboda tura sojoji Nijar ba shi ne mafita ba.
Dalilai Guda 10 da DSS ta bayar kin Amincewa da El-Rufai a matsayin Ministan Tinubu
BBC ta rawaito yan majalisar ƙasar ɓangaren marasa rinjaye sun ce abin da ya kamata a yi shi ne bin hanyar diflomasiyya da kuma tattauna.
“Ba abu mai kyau bane tura sojojin Ghana zuwa Nijar domin zub da jini, kuma muddin ba a yi hankali, abin zai sake jefa yankin cikin tashin hankali,” in ji Mista Ablakwa.
Ƴan majalisar sun ce ya kamata a yi amfani da kuɗin da ake da shi wajen warware matsin tattalin arziki da ƙasar ke fusknta baya nciyo rancen $3b daga Asusun IMF maimakon tura sojoji zuwa faɗa.