Da dumi-dumi: Ganduje ya baiwa tsohon kwamishinansa mukami

Date:

Daga Hafsat Lawan Sheka

 

Sabon shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dr Abdullahi Ganduje, ya nada tsohon kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar Kano, Muhammed Garba, a matsayin shugaban ma’aikatansa.

 

An bayyana nadin ne a cikin wata sanarwa da mai daukar hoton shugaban jam’iyyar APC na kasa Aminu Dahiru ya fitar.

Talla

Baya ga yin aiki a gwamnatin Ganduje a Kano na tsawon shekaru takwas, Muhammad Garba ya kuma rike mukamin sakataren yada labarai na ofishin mataimakin kakakin majalisar wakilai.

Da dumi-dumi: Tinubu ya ba da umarnin sake ƙaƙaba wa Nijar takunkumai

Garba ya kuma kasance tsohon shugaban kungiyar ‘yan jarida ta kasa (NUJ). Ya kuma taba zama sakataren yada labarai na ofishin mataimakin kakakin majalisar wakilai.

Tsohon kwamishinan yada labaran dai sun jima tare da tsohon gwamnan jihar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje wanda kuma shi ne mukami na farko da sabon shugaban jam’iyyar APC na kasa ya fara yi tun bayan rantsar da shi a mukamin a ƙarshen makon da ya gabata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...

Ciyaman din Wudil ya kaddamar da aikin gina magudanan ruwa a wasu garuruwa a yankin

Daga Maryam Adamu Mustapha   Shugaban karamar hukumar Wudil, Hon. Abba...