Zargin Zagon Kasa: NNPP ta dakatar da sakataren ta na ƙasa

Date:

Daga Abdulrashid B Imam

 

Jam’iyyar NNPP ta dakatar da sakataren ta na kasa, Oladipupo Olayokun bisa zargin yi wa jam’iyyar zagon-ƙasa.

Dakatarwar na kunshe ne a cikin wata wasika da aka aike wa Mista Olayokun, mai dauke da kwanan wata 6 ga watan Agusta mai taken; “Sanarwar dakatarwa”.

Shugabannin jam’iyar na Ward 5 na karamar hukumar Abeokuta ta Kudu a jihar Ogun ne su ka dakatar da Olayokun, wanda kuma mamba ne a kwamitin ƙoli na jam’iyyar na kasa.

Talla

Wasikar wacce ke dauke da laifukan sa, ta samu sa hannun shugabanni 25 alna shiyyar, da suka hada da sauran mambobin mazabu 25.

Da dumi-dumi: Abba Gida-gida ya yi sabbin nade-naden shugabannin ma’aikatu 15

An aikawa shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben da ya gabata, Rabiu Kwankwaso, da kuma wanda ya kafa jam’iyyar, Boniface Aniebonam, kwafi na wasikar.

Daily Nigeria ta tawaito Shugabannin sun kuma zargi Sakataren jam’iyyar da yin sakaci da aiki tare da karfafa bangaranci a cikin jam’iyyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...