Muna da yaƙinin Abba El-Mustapha zai kawo gyara a Kannywood – Baban Nura

Date:

Daga Abubakar Sa’eed Sulaiman

 

Wasu daga cikin jarumai a masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood sun fara hasashen harkar fim zata kara inganta, sakamakon yadda Gwamnan Kano ya nada kwararren jarumi a matsayin Shugaban hukumar tace fina-fine ta jihar kano.

 

” Abba El-Mustapha ya jima a wannan Masana’antar kuma yasan duk matsalolin mu don haka muna da tabbacin zai yi amfani da gogewa da kwarewarsa wajen inganta harkokin fina-finan Kannywood a Kano”.

Talla

Rabi’u Sani wanda ake yiwa lakabi da babban Nura shi ne ya bayyana hakan a wata tattaunawa da yayin da jaridar kadaura24 a Kano.

Ministoci: Dalilin da yasa Tinubu bai tura sunan kowa daga Kano ba

Baban Nura yace gwamnan jihar kano Abba Kabir Yusuf ya yi hangen nesa wajen zabo Abba El-Mustapha a matsayin wanda zai jagoranci hukumar tace fina-fine ta jiha, Saboda yadda yasan makamar aiki ga shi kuma da jajircewa wajen tsayawa gaskiya.

” Ina amfani da wannan dama wajen ta ya Abba El-Mustapha Murnar samun wannan mukamin, sannan Ina kira a gare shi da tsaya yayi aikinsa tsakani da Allah ya kuma yiwa kowa adalci wanda idan yayi haka babu Shakka ba zamu tabawa mantawa da shi ma ko bayan ya bar mukamin”. Inji Baban Nura

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito a makon da ya gabata ne gwamnan jihar kano Abba Kabir Yusuf ya nada Abba El-Mustapha a matsayin Sakataren zartarwa na hukumar tace Fina-finai da dab’i ta jihar kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...