Sojoji sun bayyana dalilan da suka sa suka yi juyin mulki a Nijar

Date:

Sojoji sun sanar da karɓe iko a Nijar a hukumance.

Wasu sojoji ƙalilan ne suka fito gidan talabijin na ƙasar suka tabbatar da juyin mulkin da suka yi.

Kakakin sojojin ƙasar Manjo Ahmadou Abdrahamane ne ya sanar da juyin mulkin.

Sun sanar da rushe kundin tsarin mulkin ƙasar, sannan kuma sun kulle duka iyakokin ƙasar baki ɗaya.

Talla

Babu dai labarin halin da Mohamed Bazoum ke ciki ya zuwa yanzu.

Amma sojojin sun bayar da sanarwar sun tuɓe shi daga muƙaminsa.

Shuwagabannin APC Na Arewa Maso Yamma Sun Amince Da Ganduje A Matsayin Shugaban Jam’iyyar Na Kasa

BBC Hausa sun rawaito sojojin sun ce sun yi juyin mulkin ne saboda halin da Nijar ke ciki na taɓarɓarewar tsaro da tattalin arziƙi.

Sun kuma sanar da dokar hana fita daga ƙarfe 10 dare zuwa 6 na safe.

Da dumi-dumi: Jami’an tsaro sun tsare shugaban Niger

Shugaban ƙasar Benin Patrice Talon wanda ke jagorantar tawagar ECOWAS na cikin ƙasar, sai dai sun gaza cimma wata yarjejeniya da masu gadin shugaban ƙasar da suka amshe mulkin.

Tun a safiyar jiya Laraba ne aka bayar da rahotannin tsare Shugaba Bazoum a gidan gwamnati, abin da ya janyo zanga-zanga daga magoya bayan Bazoum.

Sojoji sun yi harbe-harben jan kunne domin tarwatsa masu zanga-zangar.

Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya nuna rashin goyon bayan wannan ƙasarsa kan juyin mulkin.

Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya Antonio Guterres ya ce ya yi magana da Shugaba Bazoum kuma ya tabbatar masa da cewa yana da goyon bayan Majalisar.

Wannan ne juyin mulki na huɗu da aka yi a Nijar tun bayan samun ‘yancin kai da ta yi daga Faransa a 1960, kuma an ta yin yunkurin junyin mulki da yawa a ƙasar da ba su yi nasara ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnan Kano Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Gidaje

Daga Khadija Abdullahi Aliyu  Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf...

Matsalar Albashi: Gwamnatin Kano za ta tantance ma’aikata

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Gwamnatin jihar Kano ta umarci dukkan...

Gwamnonin Nigeria na yunkurin dakatar da turawa kananan hukumomi kason kudadensu

    Gwamnonin jihohin Nijeriya sun fara wani yunkuri na dakatar...

Ramadan: Cibiyar Markaz Imamu Malik ta raba kayan abinchi ga al’ummar Dorayi dake Kano

Daga Kamal Yakubu Ali   Cibiyar Markaz Imamu malik da ke...