Majalisar Dinkin Duniya ta yi Allah wadai da juyin mulkin Nijar

Date:

Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres “ya yi kakkausar suka ga sauyin gwamnati da aka samu a Nijar ba bisa ka’ida ba,” in ji kakakinsa a ranar Laraba.

Talla

Mista Guterres ya ce ya damu matuka da tsare Shugaba Mohamed Bazoum kuma ya damu da lafiyarsa, in ji kakakinsa Stephane Dujarric a cikin wata sanarwa.

Da dumi-dumi: Muhammad Bozoum ya Magantu Bayan yi Masa Juyin Mulki

BBC Hausa ta rawaito hakan na zuwa ne bayan da sojojin Nijar din suka sanar da juyin mulki a gidan talabijin na kasar, inda suka ce sun jingine aiki da kundin tsarin mulkin kasar, tare da dakatar da dukkan hukumomi da kuma rufe iyakokin ƙasar.

 

Mista Dujarric ya ƙara da cewa “Sakatare-Janar ɗin ya yi kira da a gaggauta kawo karshen duk wasu ayyukan da ke kawo cikas ga tsarin dimokuradiyya a Nijar.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...

Ciyaman din Wudil ya kaddamar da aikin gina magudanan ruwa a wasu garuruwa a yankin

Daga Maryam Adamu Mustapha   Shugaban karamar hukumar Wudil, Hon. Abba...