Majalisar Dinkin Duniya ta yi Allah wadai da juyin mulkin Nijar

Date:

Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres “ya yi kakkausar suka ga sauyin gwamnati da aka samu a Nijar ba bisa ka’ida ba,” in ji kakakinsa a ranar Laraba.

Talla

Mista Guterres ya ce ya damu matuka da tsare Shugaba Mohamed Bazoum kuma ya damu da lafiyarsa, in ji kakakinsa Stephane Dujarric a cikin wata sanarwa.

Da dumi-dumi: Muhammad Bozoum ya Magantu Bayan yi Masa Juyin Mulki

BBC Hausa ta rawaito hakan na zuwa ne bayan da sojojin Nijar din suka sanar da juyin mulki a gidan talabijin na kasar, inda suka ce sun jingine aiki da kundin tsarin mulkin kasar, tare da dakatar da dukkan hukumomi da kuma rufe iyakokin ƙasar.

 

Mista Dujarric ya ƙara da cewa “Sakatare-Janar ɗin ya yi kira da a gaggauta kawo karshen duk wasu ayyukan da ke kawo cikas ga tsarin dimokuradiyya a Nijar.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ba zaben 2027 ne a gaba na ba – Tinubu

    Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu...

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...