Bai kamata a rika hana Hukumar kare haddura ta kasa aiki a wasu titin jihohi ba – Sarkin Kano

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Mai martaba sarkin kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya shawarci gwamnati data amincewa hukumar kare haddura ta kasa (Road Safety) ta gudanar da aikinta ako wannen titi ba tare da takura musu ba.

 

Alhaji Aminu Ado Bayero, ya bayyana cewa sahhalewa hukumar ta gudanar da aikinta a kowanne titi zai karawa hukumar karfi wajen bincikar takardun motoci masu inganci da masa inganci.

Talla

 

Sarkin ya bayyana haka ne ayayin da yake karbar ayarin shugabanin gudanarwar hukumar kare haddura ta kasa reshen jihar kano karkashin jagorancin sabon kwamandan hukumar Alhaji Ibrahim Abdullahi Sallau a fadarsa.

Shuwagabannin APC Na Arewa Maso Yamma Sun Amince Da Ganduje A Matsayin Shugaban Jam’iyyar Na Kasa

Mai martaba sarkin kano ya kara da cewa yana kira da direbobi da sauran masu ababan hawa su baiwa hukumar kare haddura cikakken hadinkai da goyon baya don samun nasarar da hukumar.

Shi ma anasa jawabin sabon kwamandan hukumar Alhaji Ibrahim Abdullahi sallau yace ya kaiwa Sarkin ziyarar ne domin gaisuwar bangirma da gabatar da kansa a matsayin sabon kwamandan hukumar FRSC.

A wata sanarwa da babban Sakataren yada labaran Masarautar kano Abubakar Balarabe Kofar Na’isa ya aikowa kadaura24, yace a wani cigaban kuma Mai Martaba Sarkin ya karbi bakoncin shugabanin gudanarwar Bankin musulinci na Jaiz Bank karkashin jagorancin shugaban gudanarwar bankin Alhaji Muhammad Mustapha Bintube a fadarsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ba zaben 2027 ne a gaba na ba – Tinubu

    Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu...

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...