Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa
Kungiyar Kwadago ta Najeriya NLC, ta baiwa gwamnatin tarayya wa’adin kwanaki bakwai na janye duk wasu tsare-tsaren da suka jefa talakawa cikin mawuyacin hali, ciki har da karin farashin man fetur da aka yi a baya-bayan nan, ko kuma ta fuskanci yajin aikin gama gari daga ranar 2 ga watan Agusta.

Kungiyar kwadago ta NLC ta umurci dukkanin rassanta dake jihohi da su gaggauta fara haɗa kan ma’aikata da sauran ’yan Najeriya da suka hada da kungiyoyin farar hula don gudanar da yajin aikin da za a dade an yi tare da zanga-zanga idan gwamnati ta gaza biyan bukatunta.
Kansilolin 11 daga karamar hukuma daya sun fice daga jam’iyyar APC a Kano
An tattaro cewa wannan na daya daga cikin shawarwarin da aka cimma a taron kwamitin koli na NLC, wanda aka gudanar a ranar Talata, 25 ga watan Yuli a gidan ma’aikata na Abuja.
Idan dai za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito a makon da ya gabata ne gwamnatin tarayya ta sanar da karin kudin farashin man fetur daga 540 kowacce lita zuwa Naira 617 kowacce lita, wanda hakan yasa al’ummar ƙasar suke ta kokawa wasu kuma suka ajiye ababen hawansu saboda tsadar man fetur din.