Kansilolin 11 daga karamar hukuma daya sun fice daga jam’iyyar APC a Kano

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

Zababbun Kansilolin 11 na karamar hukumar Sumaila sun bayyana ficewarsu daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar NNPP Mai kayan marmari bisa wasu dalilai da suka zaiyana.

Cikin wata wasika mai dauke da kawanan watan 04 ga watan Janairu 2023 kansilolin su 11 sun ce sun bar jam’iyyar ne saboda rashin girmama su da Shugaban karamar hukumar ke yi.
Talla
Wasikar Mai dauke da sa hannun dukkanin kansilolin sun ce Shugaban karamar hukumar ta Sumaila yana tsangwamar su tare da yin halin ko un kula da lamarin su.
” Mu kansilolin karamar hukumar Sumaila mu goma Sha daya 11 na mazabu 11 mun fita daga jam’iyyar APC mun koma jam’iyyar NNPP, sakamakon tsangwama da halin ko in kula daga shugaban karamar hukumar Sumaila da Kuma da Kuma wulakanta yan jam’iyyar na mazabun mu”.
Talla

Kansilolin da suka hanya hannu akan wasikar dune Shugaban kansilolin Mustapha Garba Haladu (Council Leader), Umar Ibrahim Umar mataimakin Shugaba , Nuhu Ado Gala Shugaban masu rijaye da kuma mai tsawatarwa a majalisar kansilolin Abubakar Ahmed .

Sauran kansilolin sune Isma’il Sabi’u Salisu, Ibrahim Abubakar, Ma’amiru Nuhu, Atiku Idris, Umar Abdulsalam, Sule Adamu, and Danjuma Saleh.

Ga wasikar da suka rubuta

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...