DAGA KAMAL UMAR KURNA
An bayyana Alhaji Lawal Kolo Geidam a matsayin cikakken Dan kishin kasa Wanda Kuma ya sadaukar da lafiyarsa da lokacin sa wajen zagaye dukkanin jihohin dake arewacin Najeriya domin hado kan Malaman makarantun gaba da sakandire da masana a jihohin domin marawa takarar Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da Kashim Shattima lokacin yakin neman zabe har aka kai ga nasara.
Shugaban kungiyar gamayyar Malamai da Masanan ta kasa Dr Sulaiman Isyaku Muhammad, ne ya bayyana hakan a wajen taron da kungiyar ta shiryawa kungiyoyi irin ta a birnin tarayya Abuja, domin shirya yadda za’a bada lambar yabo ga Alhaji Lawal Kolo Geidam bisa irin gudunmawar daya bada har Shugaba Tinubu da Kashim Shattima suka Kai ga nasara.

Dr Sulaiman yace samun mutane irinsu Alhaji Lawal Kolo Geidam a tsakanin al’umma abu ne Mai matukar tasiri duba da yadda yake sadaukar da Kansa da komai nasa domin ganin al’ummar arewacin kasar nan sun samu kyakkyawar makoma da ingantacciyar rayuwa daga gwamnatin tarayya.
Da dumi-dumi: Shugabannin Jam’iyyar NNPP 9 Sun Fice Daga Jam’iyyar
Wasu daga cikin ‘yan kungiyoyi daban daban da suka halarci taron bada lambar yabon ga Alhaji Lawal Kolo Geidam sun bayyanawa jami’in yada labaran kungiyar ta Malamai da Masanan dake makarantun gaba da sakandiren kasar nan Kamal Umar Kurna cewa bawa kolo lambar yabon na a matsayin Wani salo na nuna gamsuwa da rawar da ya taka a baya yake Kuma cigaba da takawa har a yanzu domin inganta rayuwar al’ummar jihohi 19 dake arewacin kasar nan.