NEMA ta buƙaci gwamnoni su zauna cikin shiri kan yiwuwar samun ambaliya

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

 

Shugaban Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Nigeria NEMA, Ahmed Habib ya shawarci gwamnonin Kasar da su samar da cibiyoyin bayar da agajin gaggawa a jihohinsu domin kare afkuwar ambaliya.

 

“Idan gwamnonin za su bai wa hukumar haɗin-kai da kuma karɓar shawara, to ba za a iya rage asarar da aka samu a bara”.

Talla

Shugaban Hukumar ya bayyana haka ne bayan wani zama da ya yi da wasu gwamnoni a Abuja, babban birnin Nigeria.

Mun tantance mutane 800 cikin 1200 da suka nemi shiga shirin tura ɗalibai kasashen waje – Gwamnatin Kano

Ya kuma bukaci gwamnonin da su wayar da kan mutane kan muhimmancin komawa yankunan da ba su da haɗarin fuskantar ambaliya domin kare asarar rayuka da kuma dukiyoyi da sauransu.

Habib ya kuma ce akwai bukatar a taimakawa hukumar da kuɗaɗe saboda hakan zai taimaka wajen kare afkuwar bala’o’i da za a iya samu.

A makon da ya gabata ne, NEMA ta yi hasashen cewa za a iya samun ambaliya a jihohi14 na faɗin Najeriya sakamakon mamakon ruwan sama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...