Daga Kamal Umar Kurna
Shugaban kwamitin karta kwana na kwashe sharar jihar Kano Amb. Alhaji Ahmadu Haruna Zago ya sha alwashin cigaba da sadaukar kan sa wajen ganin jihar nan ta samu habaka da Samar da kyakkyawan yanayi domin da cewa da manofofin gwamnatin Injiniya Abba Kabir Yusif.

Amadu Danzago ya bayyana hakan ne lokacin da kungiyar ‘yan asalin jihar Kano masu tsaftar muhalli suka Mika masa shaidar girmamawa bisa namijin da kokarin da kwamitinsa yayi na kwashe sharar dake jibge a wasu yankunan jihar kano cikin kankanin lokaci.
Hotuna: yadda Sarkin Bichi ya gudanar da hawan ƙarshe
Dan zago yace tsaftace Muhalli da titunan jihar nan nada alaka ta kai tsaye da Samar da ingantacciyar lafiya ga al’umma, a don zai cigaba da bada dukkan lokacin sa wajen kwashe sharar.
A jawabinsa tunda fari shugaban kungiyar Dr. Bala Mohammed yace sun baiwa Dan zago shaidar girmamawar ne duba da yadda cikin kankanin lokaci kwamitinsa ya Samar da yanayi mai kyau a mafi yawan titunan jihar kano.
“Na mijin kokarin da ka yi wajen tsaftace jihar kano shi ne dalilin da yasa kungiyarmu ta amince da baka wannan matsayi na uban kungiyarmu domin samun nasarar da aka Sanya a gaba”. Inji Dr. Bala Mohammad