Babu Kwamishina da za a rantsar ba tare da bayyana kadarorinsa ba – Abba Gida-gida

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

 

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya umurci dukkan wadanda aka tura sunayen su domin nada su a matsayin kwamishinoni da su tabbatar sun bayyana abubun da suka mallaka ga hukumar kula da da’a ma’aikata ta kasa.

 

“Ana sa ran wadanda aka zaba za su bayyana kadarorinsu a cikin mafi kyawun lokaci kafin a fara tantance su a majalisar dokokin jihar a ranar Alhamis 22 ga watan Yuni, 2023 da karfe 10 na safe a harabar majalisar dokokin jihar”.

Da dumi-dumi: Abba Gida-gida ya Magantu kan baiwa dansa mukami

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban Sakataren yada labaran gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa kadaura24.

Matakin da gwamnan kano ya dauka akan albashin ma’aikatan abun a yaba ne – Anas Abba Dala

Gwamnan ya sha alwashin babu wani kwamishina da za a rantsar da shi a matsayin memba na majalisar zartarwa ta jihar kano ba tare da ya cike fom din bayyana kadarorinsa ga hukumar kula da Da’ar Ma’aikata ba.

“Duk sauran masu rike da mukaman siyasa a karkashin wannan gwamnati su ma za su bi wannan umarnin .”

Tallah

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jaddada aniyarsa ga mutanen jihar Kano na gudanar da komai a bayyane kamar yadda yake cikin manufofin da ya bayyana yayin yaƙin neman zaɓen 2023.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...