Tsohon dan majalisar tarayya a kano ya rabawa manoma sama da 400 takin zamani

Date:

Daga Safiyanu D Jobawa

 

Tsohon dan majalisar tarayya wanda ya wakilci kananan hukumomin Kura/Madobi/Garun mallam, Hon Kabiru Idris Danhassan ne ya bayyana cewa ba zai taba mantawa da al’ummarsa ba duk da baya kan wata kujerar mulki.

 

Kabiru Danhassan ya bayyana hakan a wajen mika tallafin Takin zamani a garin Karfi dake karamar hukumar Kura.

Da dumi-dumi: Abba Gida-gida ya yi sabbin nade-naden mukamai

Yace ya raba takin don tallafawa manona sakamakon muhimmancin da noma ke da shi a cikin al’umma, musamman a yankin kura madobi da garum mallam.

Dama a baya na raba irin wannan takin lokacin Ina wakiltarku, to yanzu ma da bana wakiltarku ba zan bar ku haka nan ba, zan cigaba da amfani da dan abun da nake da shi waje tallafa muku akan abun da kuka shahara akansa shi ne noma”. Inji Danhassan

Tallah

Daga bisa ni ya godewa al’ummar wadan nan yankuna bisa sahale masa wakilcinsu a majalisar tarayya, sa’annan ya yi alkawarin cigaba da rike musu amana har tsawon rayuwa. Kuma ya ce zai cigaba da irin wadan nan abubuwan alheri lokaci-lokaci.

Sama da buhu takin-zamani dari-hudu (400) a ka raba wa manoman yankunan na Kura/Madobi/Garun mallam a ranar a jiya asabar .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...