Daga Khadija Abdullahi Aliyu
Ana zargin wani bangare a ginin Tsohuwar Daula da Gwamnatin Jahar Kano ta rushe ya fada kan wasu Matasa masu diban Rodi.
Idan za’a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito cewa gwamnatin jihar kano ta rushe ginin da akai a tsohuwar Daula Otal a makwani biyu da suka gabata saboda zargin anyi ginin ba bisa ƙa’ida ba.
Yanzu-Yanzu: Tinubu ya kaddamar da majalisar tattalin arzikin Nigeria
Yanzu haka dai Jami’an Hukumar kashe Gobara da ta bada Agajin Gaggawa ta Kasa NEMA na yunkurin zakule Mutanen daga baraguzan ginin.
Da dumi-dumi: Abba Gida-gida ya bayyana ranar da zai mikawa majalisa sunayen kwamishinonini
Jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano SFS Saminu Yusuf Abdullahi ya tabbatarwa jaridar kadaura24 faruwar lamarin.
Ya kuma ce tuni jami’an hukumar su sun Isa wajen domin ceto wadanda lamarin ya faru da su, ya kuma bayyana cewa tuni sun Sami nasarar ceto mutane 3 daga cikin baraguzan ginin.
” Tuni jami’anmu sun ceto mutane uku kuma wadanda lamarin da ya faru a kan idansu , sun tabbatar mana da cewa akwai ragowar mutane da suke ciki don haka muna cigaba da bincikawa,Amma dai har yanzu bamu Sami wanda ya rasa ransa ba”. A cewar Saminu Yusuf Abdullahi