Da dumi-dumi: Majalisar dokokin Kano ta Amincewa Abba Gida-gida ya nada Masu bashi shawara 20

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Majalisar dokokin jihar Kano ta amincewa gwamnan kano Abba Kabir Yusuf ya nada masu ba shi shawara na musamman guda 20.

 

Majalisar dokokin jihar Kano ta amince da nadin mukamai na musamman guda ashirin da gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi.

Yanzu-Yanzu: Gwamnatin Kano ta bayyana dalilin da yasa ta rushe shatale-talen gidan gwamnati

Jaridar kadaura24 ta ruwaito cewa an amince da amincewar ne a yayin wani zama da shugaban majalisar, Ismail Jibrin Falgore ya jagoranta kamar yadda sashi na 196/2 na kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya ya tanada.

Hotuna: yadda Aka rushe shatale-talen dake Kofar gidan gwamnatin kano

Sanarwar da Babban Sakataren Yada Labarai na Majalisar, Uba Abdullahi ya fitar ta ce amincewar ta biyo bayan wasikar da Gwamnan ya aike wa majalisar na neman nadin wanda aka tattauna a gaban zauren majalisar tare da cimma matsaya.

Majalisar ta dage zamanta zuwa ranar 19 ga watan Yuni, 2023 a wani kudiri da shugaban masu rinjaye Hon Lawan Husaini na mazabar Dala ya gabatar kuma ya samu goyon bayan shugaban marasa rinjaye Labaran Abdul Madari wakilin karamar hukumar Warawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...