Da dumi-dumi: Akwai yiwuwar ni zan mika mulki ga sabon gwamnan kano – Ganduje

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Gwamnan jihar kano mai barin gado Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya ce Akwai yiwuwar shi da kansa ne zai mika jihar ga sabon zaɓaɓɓen gwamnan jihar Engr. Abba Kabir Yusuf a yau Lahadi.

 

” Muna nan Muna tuntubar juna kan yadda zan mika Kano ga sabuwar gwamnati, idan mun cimma matsaya ni da kai zan mika mulkin, idan kuma yanayi bai bada dama ba to Sakataren gwamnatin jihar kano shi zai mika musu mulkin kamar yadda doka ta tanada”. Ganduje

Kadaura24 ta rawaito Gwamna Ganduje ya bayyana hakan ne lokacin da yake jawabin bankwana ga al’ummar jihar kano a daren jiya asabar.

Ganduje ya bude gidan wutar lantarki mallakin kano

Ganduje ya kara da cewa kasancewa dukkanin bangarorin biyu na gwamnati mai barin gado da Kuma gwamnati mai jiran gado suna cikin uzurori daban-daban don haka ya ce idan hali yayi zai mika mulkin a Cikin daren wannan rana ta Lahadi.

Ganduje ya godewa al’ummar jihar kano bisa yadda suka bashi hadin kan da suka bashi har ya gudanar da aiyukan raya kasa da cigaban al’umma a tsahon shekaru 8 da yayi yana mulkin jihar.

” Da jam’iyyar mu ta APC ce zata gajemu da zan halarci bikin rantsuwar kama aiki na sabuwar gwamnati, Amma tunda Babu kyakyawan yanayi ba za’a ganmu a wajen bikin ranar rantsuwa ba, duk da dama kundin tsarin mulki bai ce dole sai gwamna mai barin gado yana wajen ba”. Inji Ganduje

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...