Da dumi-dumi: Kotun Sauraren Kararrakin Zaɓe ta Kori Koken da aka shigar akan Tinubu

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa ta yi watsi da karar da jam’iyyar Action Peoples Party (APP) ta shigar na kalubalantar zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu.

 

A ranar Laraba ne kwamitin shari’a mai mutane biyar karkashin jagorancin Mai shari’a Haruna Tsammani ya yi watsi da batun bayan da jam’iyyar ta sanar da janye karar ta.

A zaman da aka ci gaba da sauraron karar, lauyan APP, Obed Agu Esq ya bayyana cewa jam’iyyar da dan takararta na shugaban kasa, Simon Nnadi, sun yanke shawarar janye karar.

DA DUMI DUMI: Kotun Sauraren Kararrakin Zaɓe ta ɗage Shari’ar da ake Kalubalentar Tinubu Zuwa Alhamis

Sai dai bai bada wani cikakken dalili ba.

A zaman farko da kotun ta yi a ranar Litinin, a yayin zama share faggen sauraron karar Agu ya bukaci kotun da ta tilasta wa Tinubu da APC su aminca cewa ba su suka yi nasara a zaɓen ba, saboda yadda APC suka tafka magudi a zaben .

Sai dai lauyoyin APC da Tinubu, Lateef Fagbemi da Wole Olanipekun, manyan Lauyoyin Najeriya, sun sanar da kotun da za ta yi maganin matsalolin a lokacin da ya dace.

Jam’iyyar a cikin karar ta bukaci kotun da ta soke takarar, Bola Tinubu bisa zargin rashin cancantar sa na tsayawa takara Shugaban kasa.

Sun kuma bayyana cewa INEC ta gaza yin aiki da dokar zabe ta 2022 ta tanada, ta hanyar hana fitar da sakamakon zabe, wanda hakan ya sa su yi nasara a zaben, inda suka kara da cewa an sami cin hanci da rashawa a zaben .

Sun kuma kara da cewa APC da Tinubu ba su samu rinjayen kuri’un da aka kada a zaben ba, wanda ya hada da tilascin samun kashi 25 na kuri’un da aka kada a babban birnin tarayya Abuja.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...