Gobara ta lalata kaya na miliyoyin nairori a wata kasuwa da ke Zaria

Date:

 

Akalla shaguna 150 ne ake zaton gobara ta lalata a kasuwar ƴan Katako da ke garin Zariya a jihar Kaduna.

 

Rahotanni sun bayyana cewa gobarar ta tashi ne da misalin karfe 1 na dare lokacin da mutane ke barci.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito shugaban masu samar da tsaro na kasuwar, Hamisu Buhari na cewa gobarar ta tashi ne lokacin da hukumar samar da wutan lantarki da KEDCO ta dawo da wuta, inda wani igiyar wutar lantarki ta faɗa kan ɗaya daga cikin shagunan.

Da dumi-dumi: Kwankwaso ya zama mai baiwa gwamnan kano Abba Gida-gida shawara akan Ilimi

Ya ce daga nan ne kuma wutar ta yaɗu zuwa sauran shaguna da ke cikin kasuwar, inda ya ce duk wani kokari na kiran jami’an kahse gobara ya citura.

Hukumar Yan Sanda ta turo sabon kwamishinanta kano

Ya ƙara da cewa gobarar ta ƙona shaguna sama da 150 kurmus da kuma asarar dukiya ta miliyoyin naira.

Da aka tuntuɓi shugaban hukumar ta KEDCO, Abdul Azeez Abdullahi, ya musanta cewa wutar lantarki ce ta jawo tashin gobarar.

A baya-bayan nan dai ana samun tashin gobara a yawancin kasuwa da ke faɗin Najeriya, inda ake asarar dukiya ta miliyoyn naira.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...