FCE Bichi na daf da durkushewa, saboda matsalolin da suka yi yawa a makarantar – Dr. Hussaini Peni

Date:

Daga Abubakar Lawan Bichi

 

Kungiyar Mallaman Kwaleji Ilimi ta Tarraya dake Bichi wato COASU ta shiga yaji aiki sai baba ta gani, Sakamakon lalacer abubuwan a Makarantar da rashin iya gudanar shugabanci na shugaban Makarantar Professor Bashir Muhammad Fagge.

 

Shugaban Kungiyar ta COASU DR. Hussaini Yahaya Peni da Sakataren Moji Kenneth Terngu Suka bayyana haka yayi Ganawarsu ga manema labarai a Cibiyar Kungiyar Yan Jaridu dake nan Kano.

Yan takarar majalisar jiha na NNPP su 9 a Kano sun yi karar APC, INEC a Kotun sauraren kararrakin zabe

 

Dr. Hussaini Yahaya Peni ya ce makarantar ta dauki hanyar durkushewa saboda dakunan Gwajegwaje Kimiya da Fasaha na Makarantar sun lalace, basa yin aiki sakamakon rashin kulawa daga hukumar Makarantar ta FCE Bichi.

Zaɓen Gwamnan Kano: APC ta roki kotun sauraren kararrakin Zabe har abubuwa guda 5

 

Dr. Peni ya kuma fargabarsa na amkuwar aiyukan ta’addanci sakamakon rashin Tsaro a Makaranta Saboda rashin kulawa na Shugabanci Makarantar na yanzu.

 

Dr. Hussaini Yahaya Peni ya kara da cewar Ma’ikata a makaranta sun zama koma bayan sakamakon rashin biyansu hakokinsu, rashin biyan Kudade taimakekeniyar Lafiya, da rashin saka kudade da ake yankewar Ma’ikatar na wata-wata zuwa Asusu na MultiPurpose Cooperative da kuma dukkanin wasu H?hakkokin Ma’ikata.

 

Akwai rashin Samar da kayan karatu, lalacewar dakunan Kwanan dalibai, ajujuwan karatu da kuma rashin sakar kudade da Asusun dake tallafawa ilimi na Kasa wato TETfund ya Samar aka tsare-tsare cigaban ilimi a Makarantar Kamar horal da dalibai Sani Makamar aiki teaching practice, Samar litartafai da kuma kari sanin makamar aiki ga Mallamai.

 

Dr Hussaini Yahaya Peni yace basu da wata mafitar Sai dai su shiga yaji aiki sai baba ta gani domin ceto makarantar daga durkushewa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...