Amurka ta ƙara wa ‘ƴan Najeriya kuɗin neman takardar visa

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Amurka ta ƙara yawan kuɗin da take karɓa daga masu neman takardar izinin shiga ƙasar ga masu son zuwa yawon buɗe ido da kuma karatu.

 

A wata sanarwa ta ma’aikatar hulɗa da ƙasashen wajen Amurka, ƙasar ta ƙara yawan kuɗin masu neman takardar shiga ƙasar zuwa dala 185 daga 160.

 

DSS ta ce ta gano makarkashiyar kafa gwamnatin rikon kwarya a Nigeria

Sanarwar da aka wallafa ranar 28 ga watan Mayu ta ce ƙarin zai fara aiki ne daga yau 30 ga watan Maris, 2023.

 

Haka nan an yi ƙarin kuɗin a kan masu neman takardar shiga ƙasar domin waɗansu abubuwan na daban, kamar aikin da kuma masu zuba jari.

Mutane biyar sun ƙone ƙurmus a hatsarin mota a Bauchi

 

Amurkar ta ce ta yi hakan ne domin inganta yadda take bayar da takardar shiga ƙasar ga baƙi da kuma ƴan ci-rani.

 

Kuma sanarwar ta ce an yi ƙarin ne ta hanyar la’akari da kuɗin da ake kashewa wajen samar da takardun.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: Bam ya fashe a Kano ya hallaka wasu ya kuma jikkata wasu

Aƙalla mutum biyar ne aka tabbatar da rasuwarsu, yayin...

Kotu a Kano ta sami wani Tela da laifin takurawa makwabtansa da karar keken dinki

Wata kotu a Kano ta samu wani tela da...

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...