Saudiyya ta gargaɗi masu ɗaukar hoto a lokacin ziyarar ibada

Date:

 

Hukumar kula da aikin Haji da Umrah ta Saudiyya ta yi kira ga masu ziyarar ibada zuwa wurare masu alfarma da su martaba darajar wuraren.

 

Sannan kuma su bi dokoki wajen ɗaurar hotunan.

 

Hukumar ta ce bai kamata masu ziyarar ibadar su ɓige da ɗaukar hotuna, a maimakon mayar da hankali kan ibadar da ta kai su ƙasa mai tsarkin.

 

Haka kuma hukumar ta gargaɗi masu ɗaukar hotunan da su guji haɗawa da wasu mutanen a cikin hoton nasu, ba tare da izini ba.

 

Sannan ta bayyana cewar masu ziyarar ibadar su daina tsayawa don ɗaukar hoto a wuraren da jama’a da dama suka taru, domin a cewarta hakan na janyo cunkuson jama’a a wuraren.

 

A baya-bayan nan dai mutane sun ɓullo da salon ɗaukar hotuna a lokacin ziyarar ibada zuwa ƙasa mai tsarkin tare da wallafawa a shafukansu na sada zumunta.

 

Lamarin da wasu malamai ke ganin cewa zai iya zama ‘Riya’, abin da kuma a cewar malaman zai iya ɓata wa mutanen ibadar tasu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...