INEC ta saka ranakun bai wa zaɓaɓɓun gwamnoni takardar shaidar cin zaɓe

Date:

Daga Maryam Ibrahim Zawaciki

Hukumar zaɓe mai zaman kanta a Najeriya ta ce ta saka ranakun da za ta bayar da takardar shaidar cin zaɓe ga zaɓaɓɓun gwamnoni a jihohin ƙasar da aka gudanar da zaɓen gwamna.

A wata sanarwar da hukumar INEC din ta fitar mai ɗauke da sa- hannun shugaban kwamitin yada labarai da ilimantar da masu kada ƙuri’a na hukumar Festu Okoye, ta ce sashe na 72 (1) na dokar zaɓen ƙasar ta 2022, ya ɗora wa hukumar alhakin bayar da takardar shaidar cin zaɓe ga zaɓaɓɓun ‘yan takara a cikin kwana 14 da yin zaɓen.

Magauta sun Saka ni a gaba – Donald Trump

A kan haka ne hukumar ta ce ta saka ranar Laraba 29 ga watan Maris da kuma 31 ga watan na Maris a matsayin ranar da za ta bayar da takardar shaidar cin zaɓen ga zaɓaɓɓun gwamnoni da mataimakansu, tare kuma ‘yan majalisun dokokin jihohi.

Oladipo Diya tsohon shugaban sojin Nigeria ya rasu

Sanarwar ta ce za a bayar da takardar shaidar cin zaɓen ne a harabar ofisoshin hukumar da ke faɗin jihohin ƙasar.

Hukumar zaɓen ta ce kwamishinonin INEC na jihohi da ma’aikatan hukumar za su sanar da zaɓaɓɓun takamammiyar ranar da za su karɓi takardun shaidar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...