Kwankwaso ya kokan kan jinkirta fadar sakamakon Zaɓen Kano

Date:

Daga Maryam Muhd Danali

 

Tsohon gwamnan jihar kano Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya koka tare da yin zargin ana Shirin kwace musu zabe.

 

Sanata Kwankwaso ya bayyana hakan ne ga yan jaridu a gidan sa dake Miller Road a Kano.

 

Yace suna Zargin ana Shirin yi musu abun da akai musu a zaɓen 2019 Inda aka ayyana zaben a matsayin wanda bai kammala ba, saboda wasu dalilai.

” To yanzu ma ga shi an lissafa kuri’un jam’iyyar mu ta NNPP ta ci zabe amma wai baturen zaɓen ya ki fadar sakamakon ya ma Kara lokacin, wannan Wani shiri suke yi na cutar da al’ummar jihar kano”. Inji Kwankwaso

 

Kwankwaso yace bisa alamu al’ummar jihar kano zasu wayi gari cikin bakin ciki saboda abun da hukumar zabe take shirin yi, wanda ya sabawa abun da mutanen kano suka zabe.

 

” Yanzu zaka gani gobe cewa zasu yi kowa kar ya fito saboda sun San abun da sukai Abu ne da bai kamata ba, ban taba ganin zabe irin wanann ba , mutane sun ce ga wanda suke so, Amma Yanzu suna shirin canja abun da aka zaba”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...