Zaben kano: Rundunar yan sanda ta sake turo sabon Kwamishina jihar kano

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Babban sifeton yan sanda, Usman Alkali Baba, ya turo CP Ahmad Kontagora, zuwa Kano a matsayin sabon kwamishinan yan sanda da zai jagoranci gudanar da zaben gwamna da na yan majalisar dokoki na jiha.

 

Wannan ya biyo bayan dakatar da turo CP Feleye Olaleye, da babban sifeton yan sandan ya yi, bayan an turo a makon da ya gabata a kwamishinan yan sandan jihar.

 

Amma a wata takardar da aka fitar ranar Litinin mai lamba TH.5361/FS/FHQ/ABJ/SUB.6/144, Babban Sufeton yan sandan yace CP Ita Lazarus Uko-Udom zai cigaba da kula da Kano ta Tsakiya, kamar yadda  Daily Nigerian ta ruwaito.

 

Ku Karanta: Da dumi-dumi: Bayan hukuncin kotun koli CBN ya Magantu akan amfani da tsofaffin kuɗi

Yayin da sanarwar ta umarci  DCP Abdulkadir El-Jamel don kula da kananan hukumomin Albasu, Gaya, Rogo, Takai, Ajingi, Garko, Wudil da Sumaila.

 

 

DCP Adamu Ngojin zai kula da kananan hukumomin Rano, Bebeji, Bunkure, Doguwa, Kiru, Kibiya Tudunwada dake Kano ta Kudu.

Ku Karanta: Gobara ta kone Shaguna da dama a Kasuwar Singer dake Kano

 

IGP din ya kuma ci gaba da rike DCP Abaniwonda Olufemi zuwa Kano ta Arewa, inda ACP Adamu Sambo a matsayin wanda zai dafa masa.

 

 

A sabuwar siginar, DCP Auwal Musa zai ci gaba da rike mukaminsa na DC CID, yayin da DCP Aminu Maiwada aka maye gurbinsa da DCP Nuhu Darma a matsayin DC Operations a Rundunar yan sandan Kano.

 

 

A yan kwanakinnan dai rundunar yan sandan ta turo kwamishinonin yan sanda akai-akai zuwa jihar Kano, wanda ya janyo korafi da gudanar da zanga-zanga daga magoya bayan jam’iyyar adawa ta NNPP, sakamakon yunkurin turo tsohon babban jami’in tsaron gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje wato CP Balarabe Sule, wanda shi ma aka dakatar da turo shi.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...