Zaɓen 2023: Za a rufe kasuwanni a ranar Asabar domin fita zaɓen shugaban ƙasa

Date:

Za a rufe kasuwanni da kuma shaguna a gobe Asabar a daidai lokacin da ‘yan Najeriya ke shirin fita rumfunan zaɓe domin kaɗa kuri’a a zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar tarayya.

Talla

‘Yan sanda sun bayar da sanarwar cewa za a takaita zirga-zirga a faɗin ƙasar a ranar Asabar har na tsawon sa’a 18, inda masu ayyuka na musamman kaɗai za a bari.

Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil

‘Yan Najeriya za su fita ne kawai zuwa rumfunan zaɓe, inda daga bisani bayan kaɗa kuri’a, za su koma gida.

A jihar Kano, mutane da dama na ta sayan kayan abinci gabanin zaɓukan ƙasar da aka daɗe ana jira saboda kasancewa babu zirga-zirga a ranar Asabar, inda ‘yan ake sa ran sai an sanar da sakamakon zaɓen kafin yawancin ‘yan kasuwa su koma wuraren kasuwancinsu.

Wani mai suna Shuaibu, ya faɗa wa BBC cewa zai saya wa iyalansa abincin da za su ɗauki tsawon kwanaki suna amfani da shi kamar yadda ya saba yi a zaɓukan baya.

“Kullum akwai rashin tabbas game da zaɓe a nan, don haka abu mafi kyau shi ne a shirya shi da isasshen abinci a gida,” in ji Shuaibu.

Ana sa ran zaɓen shugaban kasar da za a gudanar, zai kasance mai zafi wanda ba a gani cikin shekaru da dama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...