Rundunar yan sanda a Kano ta kama ‘yan bangar siyasa 85

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ta kama mutane 85 waɗanda ta ke zargin ‘yan bangar siyasa ne tare kuma da ƙwato muggan makamai.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar , SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, ta ce suna ci gaba da binciken mutanen da suka kama.

Talla

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, ya gode wa al’umma jihar bisa haɗin-kai da suke bai wa rundunar, inda ya roki goyon bayansu wajen ganin an gudanar da zaɓe mai gaskiya a Najeriya.

Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil

A jiya ne dai aka samu rikici lokacin da magoya bayan jam’iyyar NNPP suka je tarbar ɗan takarar shugaban ƙasar na jam’iyyar, Injiniya Rabi’u Musa kwankwaso a jihar Kano lamarin da ya janyo jikkatar mutane da dama tare da ƙona motoci.

Jam’iyyar NNPP na zargin ‘yan jam’iyyar APC da kai musu harin a yayin da ‘yan APCn kuma suka musanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...