Hukumar kidaya ta shiryawa yan jaridu bita kan aiyukan kidiyar bana

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Hukumar kidiya ya kasa ya bukaci yan jaridu da su baiwa hukumar hadin kai domin samun nasarar gudanar da kidiyar da zata gudanar a wannan shekara.

Kadaura24 ta rawaito Kwamishinan hukumar a nan Kano Dr. Isma’il Lawan Sulaiman ne ya bayyana hakan yayin wata bita yini guda da hukumar ta shiryawa yan jaridu a Kano .
Talla
Kwamishinan yace yan jaridu yana da gagarumar gudunmawa da zasu baiwa hukumar wajen nan hukumar ta Sami nasarar gudanar da kidayar ta bana .
Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil
” Kamar yadda muka shirya muku wannan bitar hakan sauran hukumomin irin namu na jihohin kasar nan sun shiryawa abokan aikin ku irin wannan bitar, Kuma fadakar da ku abubuwan da zamu yi don haka muna bukatar hadin kan ku domin mu Sami nasarar gudanar da kidayar” . Dr. Isma’il Lawan
Yace kidayar bana ta banbanta da wadanda aka taba yi a kasar nan, saboda za a yi ta ne da na’urar zamani, don tafiya dai-dai da zamani da kuma tafiyar da kidayar kasar nan daidai da tanadin majalisar dinkin duniya.
” Yanzu haka mun kusa kammala duk wasu shirye-shiryen gudanar don gudanar da kidiyar bana , kuma wannan bita da muka shirya muku  na daga cikin shirye-shiryen da muke yi don ganin an gudanar da kidayar cikin nasara”. Dr. Isma’il Lawan Sulaiman
Dr. Isma’il Lawan ya bukaci yan jaridun dake jihar kano da su taimakawa hukumar wajen wayar da kan al’umma don su fahimci muhimmancin kidayar da alfanun da hakan ke da shi wajen cigaban kasa .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...