Ku fito ku zabi shugabannin da kuke so – Sarkin kanuri ya umarci mutanen sa Mazauna kano

Date:

Daga Rabi’u Usman

 

Shehun Borno a jihar Kano Kuma Sarkin kabilar Kanuri Mazauna kano Alhaji Mustapha Lawan (mai kanuri) yayi kira ga yan kabilar kanuri mazauna jihar kano dasu fito su yi zaben shekarar 2023 ba tare da farbar ba don sauke nauyin da kundin tsarin mulki Nigeria ya dora musu .

 

Kadaura24 ta rawaito Wakilin shehun Borno a jihar kano ya bayyana hakan ne yayin da ya kamata gana da manema labarai kan Zaben shekara ta 2023 dake tafi.

Talla
Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil

 

Sarkin ya Umarci dukkannin kabilar Kanuri mazauna kano dasu fito kwansu da kwarkwata su zabi wanda suka ga ya Chanchanta a wajen su ba tare da tashin hankali ko hayaniya ba yayin gudanar da zabukan da muke tunkara na 2023.

 

Daga nan yayi Addu’ar samun zaman lafiya ga jihar kano da Borno dama kasa baki daya.

 

A karshe yace ya zama wajibi ga duk Dan Kasa na gari ya fito ya yi zabe sannan ya baiwa Jami’an tsaro hadin kai wajen yin aikin su kamar yanda doka ta tanada.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...