Al’ummar Kano na jiran zuwan Kwankwaso domin Kamfen din Shugaban Kasa Ranar Alhamis

Date:

Daga Kamal Yahaya Zakaria
 Al’ummar jihar kano da magoya bayan jam’iyyar NNPP damasu ruwa da tsaki na jam’iyyar NNPP sun yi shirin tarbar jagoran jam’iyyar kuma dan takarar shugaban kasa a zaben 2023, Sen. Rabi’u Musa Kwankwaso wanda aka ce zai je Kano a ranar Alhamis 23 ga watan Fabrairu, 2023 domin kammala gangamin yakin neman zabensa a fadin kasar.
 Sanata Kwankwaso, ya riga ya kai ziyara jihohi 35, kuma zai Sami kyakyawar tarba ta musamman daga magoya bayansa a Kano karkashin jagorancin dan takarar gwamnan jihar NNPP a 2023, Engr. Abba Kabir Yusuf.
Talla
 A sanarwar da Sanusi Bature Dawakin Tofa, babban mai magana da yawun yakin neman zaben Abba Kabir Yusuf ya aikowa kadaura24, yace ana sa ran magoya bayan jam’iyyar NNPP za su hadu a Kwanar Dangora da ke kan hanyar Kano zuwa Zariya da karfe 10:00 na safe domin taro dan takarar.
Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil
 Masu ruwa da tsaki na jam’iyyar NNPP da magoya bayan ta sun shiga zabukan shugaban kasa da na gwamnoni da na ‘yan majalisun tarayya da na Jiha tare da fatan samun nasarar lashe zaben ganin yadda jam’iyyar ke da farin jini da karbuwar jama’a a fadin jihohin kasar nan 36.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...